Posts

Lauyan Bogi Ya Fashe Da Kuka Bayan Da Kotun Shariar Musulunci Da Ke Kurna A Kano Ta Damke Shi

Image

An Kama Karuwai Da Yan Kwaya 120 A Hills And Valley Da Ke Kano

Image
Kungiyar Hisba a jihar Kano ta sanar da kama ‘yan mata karuwai 79 da maza masu shaye-shaye 39 a wani gidan holewa mai suna Hills and Valleys Recreational Centre dake Awakin Kudu a jihar Kano. Shugaban Hisba a jihar Abba Sufi yace mata 20 daga cikin wadanda aka kama basu wuce shekara 13 zuwa 14. Yanzu dai za’a kaisu kotu domin yanke musu tara da kuma hora su.

Gwamna Umar Bindow Na Jihar Adamawa Ya Ziyarci Tsohon Gwamnan Jihar Taraba, Danfulani Baba Suntai Da Ke Fama Da Rashin Lafiya Tun Hatsarin Jirgin Da Ya Yi A Shekarar 2012.

Image

HOTUNA: A yau Alhamis, 9 ga watan Maris, shugaba Buhari ya karbi bakuncin Archbishop of Canterbury, Rev Justin Welby. Ya karbe shi ne a Abuja House da ke birnin London.

Image

Mata: Ku guje wa saka takalma masu tsini saboda illata kashin baya da yake yi - Dr Martins Adejo

Image
Wani likita a asibitin Makurdi Dr Martins Adejo ya gargadi mata da su yi taka tsantsan da saka takalman masu tsini domin ya na lahanta kashin bayan mutum. Likitan yace wadannan takalma na illata kashin baya wanda hakan ya kan lalata wasu sassan dake hade da kashin baya bayan illata kashin shi kansa. Ya kara da cewa takalma masu tsini na kawo matsala a kwiwwowi da gabobi da tafin kafa, sannan kuma yana raunana jijiyoyin dake tafiyar da jinni a jikin mutum. “ Idan mace ta nace da sa irin wadannan talkalma za ta samu matsala da jijiyoyin ta da kuma gabobin jikinta idan girma ya zo. Likita Adejo yace dalilin irin wadannan matsaloli da za’a iya samu zai iya kai ga mutum ya kamu da cutar hawan jinni da ciwon suga.

HOTUNA: Rotimi Amaechi, Lai Mohammed, Kemi Adeosun na daga cikin ministocin da su ka halarci bikin taya  mukaddashin shugaban kasa Yemi Osinbajo, murnar cika shekara 60.

Image

Bankuna 3 Sun Kwace Kamfanin Sadarwa Na ETISALAT

Image
Bankunan Guarantee Trust, Zenith da Access na shirin kwace kamfanin sadarwa ta Etisalat saboda bashin biliyoyin naira da take bin Kamfanin. Bankunan na bin kamfanin Etisalat bashin sama da naira biliyan N540. Kamfanin Etisalata na da masu amfani da layinta sama da mutane miliyan 21 a wata kididdiga da akayi a watan Janairun 2017. Kamfanin ta koka da tabarbarewan tattalin arzikin kasa a matsayin dalilan da ya sa kamfanin ta gagara biyan basussukan. Wani babban darekta a hukumar NCC yace hukumar ta yardan ma bankunan da su kwace kamfanin a matsayin bashinsu.