An Kama Dan Nijeriya Da A Ke Zargi Da Shirya Harin Ta addanci A Jamus

'Yan sanda a nan Jamus sun kame wasu mutane biyu daya dan kasar Aljeriya daya kuma dan Najeriya a bisa zarginsu da shirya kai wani harin ta'addanci a cikin kasar.
An kama mutanen ne a wannan Alhamis a lokacin wani sumame da 'yan sanda 450 suka kai a birnin Göttingen na tsakiyar kasar bayan da suka samu wasu bayanan sirri da ke nuna cewar mutanen wadanda mambobin Kungiyar Musulmi Salafawa ne na shirin kitsa kai wani hari a kasar.
Mutane kimanin 550 ne masu alaka da Kungiyar Salafawa a Jamus mahukuntan kasar suka jera a jerin sunayen mutanen da ke a matsayin wata babbar barazana a kasar.
Kasar Jamus wacce sannu a hankali Musulmi masu akidar Salafanci ke yaduwa a cikinta a 'yan shekarun baya bayan nan, ta fuskanci jerin hare-haren ta'addanci wadanda Kungiyar IS ta dauki alhakin kai su.

Comments

Popular posts from this blog

Ya Tashi Tun Daga Nijeriya Har Zuwa London Saboda Ganin gidan Da Shugaba Muhammadu Buhari Ke Zaune A Ciki

An Yi Yunkurin Hallaka Sarkin Saudiyya A Malaysia