Cinikin makamai ya karu a duniya

Wani sabon rahoto da a gudanar, ya bayyana cewa ba a taba samun wani lokaci da aka yi cinikin makamai a duniya kamar dan tsakanin nan ba tun bayan yakin Duniya na biyu.
Kwararru a cibiyar Stockholm Internation Peace Research da suka fitar da sakamakon binciken, sun ce yawan makaman da aka yi cinikinsu tsakanin shekarar 2012 zuwa bara, ya tashi da kashi 8 cikin dari idan aka kwatanta da shekaru biyar da suka wuce.
Kasashen gabas ta tsakiya da kasashen Golf su ne suka fi sayan makamai a wannan lokacin, ya yin da a cikinsu Saudiyya ta fi kowacce sayan makamai, sai kuma kasar India.
Rahoton ya karkare da cewa kasashe biyar a duniya su ke fitar da kashi 75 cikin 100 makaman, wato Amurka, da Rasha, da China, da Faransa sai kuma Jamus.

Comments

Popular posts from this blog

An Yi Yunkurin Hallaka Sarkin Saudiyya A Malaysia

Ya Tashi Tun Daga Nijeriya Har Zuwa London Saboda Ganin gidan Da Shugaba Muhammadu Buhari Ke Zaune A Ciki