RIKICIN KUDANCIN KADUNA: An Sake Kashe Mutane 21 A Kaura Da Jemaa

Shugaban karamar hukumar Kaura da ke jihar Kaduna Mista Alex Iya, ya tabbatar da kisan mutane 14 a wani tagwayen hare-hare a kauyukan Mifi da Ashim da wasu ‘yan bindiga da ake zargin Fulani suka kai a safiyar yau Litinin.
Rahotanni daga karamar hukumar Jema’a na cewa, a daren jiya aka kai wani hari inda aka kashe mutane bakwai a unguwar Bakin Kogi da ke cikin karamar hukumar ta Jema’a.
Dan majalisar dokokin jihar Kaduna mai wakiltar karamar Hukumar Kaura, Dakta Yakubu Bityong ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda harin ya yi sanadiyyar rasuwar mutane 21 a yankin kudancin Kaduna, ya kuma ce, maharan sun kone gidajen jama’a da dama kafin zuwan jami’an tsaro yankin.

Comments

Popular posts from this blog

Hotuna: Kyautar Da Yan Shia Suka Ba CAN Yau A Bauchi

Hotuna: Garin Da Ya Fi Ko Wane Gari Sanyi A Duniya