Shugaba Jammeh ya tsige jakadodi 12
Rahotanni daga kasar gambiya na cewa Shugaba Yahya Jammeh ya sauke jakadun kasar 12 na kasashen ketare da suka hada da na MDD da kasashen Amirka, Senegal, China, Rasha, Birtaniya, Turkiyya. Ministan harakokin wajen kasar ta Gambiya ne ya bayyana sunayen jakadodin wadanda nan take aka bukaci su dawo gida ba tare da bayyana dalillan daukar wanann mataki ba.
Comments